Followers

Tuesday, April 7, 2020

Corona Virus Ta kashe mutum na farko a jihar Katsina

Coronavirus ta kashe likita a jihar KatsinaWallafawa ranar: Chanzawa ranar: 

Wani likita a Daura da ke jihar Katsinan Najeriya ya mutu sakamakon kamuwa da cutar coronavirus, bayan ya ziyarci jihohin Kogi da Lagos. Gwamnan Jihar Aminu Bello Masari ya sanar da mutuwarsa bayan an yi gwajin samfurin jininsa a birnin Abuja wanda ya tabbatar cewa cutar ta coronavirus ta kashe shi.
Aminu Bello Masari kan mutuwar likita a Daura bayan fama da coronavirus .
Masari ya ce, tuni suka  tashi tawagar likitoci zuwa garin Daura domin diddigin mutanen da likitan ya yi hulda da su da zummar yi musu gwaji da kuma killace su saboda fargabar cewa, su ma sun kamu da wannan annoba.
Ana iya cewa wannan ne karo na farko da cutar coronavirus ke kisa a Jihar Katsina da ke Najeriya.

Mun Kwafo daga shagin rfi
Hausa

No comments:

Post a Comment